Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jam’iyyar APC Ta Kalubalanci Hukuncin Kotun Kano Akan Ganduje


Tsohon Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje (Facebook/Gwamnatin Kano)
Tsohon Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje (Facebook/Gwamnatin Kano)

Jam’iyyar APC ta dauki matakin shari’a a kan mai shari’a Usman Na’abba na babbar kotun jihar Kano, inda suka mika koke ga majalisar shari’a ta kasa (NJC).

WASHINGTON, D. C. - Matakin na zuwa ne bayan da Mai Shari’a Na’abba ya bayar da umarnin hana Dr. Abdullahi Ganduje, Shugaban Jam’iyyar na kasa aiki a matsayin Shugaban Jam’iyyar.

Dokar da aka ayyana ta biyo bayan dakatar da Dr. Ganduje ne a ranar Litinin da shugabannin mazabar sa da ke karamar hukumar Dawakin-Tofa ta jihar Kano suka yi.

Mai baiwa Gwamna Ganduje shawara kan harkokin shari’a Barista Gwanjo da mataimakin sakataren unguwar, Mr. Laminu Baguma ne suka shigar da takardar.

Takardar ta bayyana sunayen APC, kwamitin ayyuka na kasa, kwamitin zartarwa na APC na jihar Kano, da kuma Dr. Ganduje a matsayin wadanda ake kara.

Bar. Haladu Gwanjo, mai ba da shawara kan harkokin shari’a na gundumar Ganduje ta APC a karamar hukumar Dawakin-Tofa a jihar Kano, ya yi wa manema labarai jawabi a Kano, inda ya sanar da dakatar da Ganduje.

Bar. Gwanjo ya bayar da misali da zargin karbar rashawa da ake yi wa Dr. Ganduje a matsayin dalilin dakatarwar, inda ya bayyana karara a kan tuhumar da gwamnatin jihar Kano ta shigar kan Ganduje a gaban babbar kotun jihar Kano da suka shafi badakalin kudi $413,000 da kuma N1.38bn.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG