Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mutane 16 Sun Rasu A Wani Hari Da Aka Kai Garin Maiduguri


Mutane sun tsere bayan harin kunar bakin waken na, Maiduguri, Najeriya, Talata, Nuwamba 25, 2014.
Mutane sun tsere bayan harin kunar bakin waken na, Maiduguri, Najeriya, Talata, Nuwamba 25, 2014.

Wata fashewa da ta auku a wata kasuwa da ake samun cunkoson jama’a yau asabar a arewa maso gabashin Najeriya ya kashe a kalla mutane goma sha shida sama da ishirin kuma suka jikkata.

Wata fashewa da ta auku a wata kasuwa da ake samun cunkoson jama’a yau asabar a arewa maso gabashin Najeriya ya kashe a kalla mutane goma sha shida sama da ishirin kuma suka jikkata.

Bom din ya tarwatse ne da misalin tsakar rana a Maiduguri babban birnin jihar Borno.Rahotanni na nuni da cewa, mai yiwuwa wata karamar yarinya yar shekaru goma ta tada shi.

Kawo yanzu babu kungiyar da ta dauki alhakin harin.

A garin Potiskum kuma, wani jami’in ‘yan sanda ya shaidawa wani dan jarida cewa, bom da ya tarwatse a wata mota da ya kashe mutane biyu, harin kunar bakin wake ne.

Kungiyar mayakan Boko Haram dake tada kayar baya a arewa maso gabashin Najeriya ta sha kai hare hare a Maiduguri da Potiskum.

Wakilinmu Haruna Dauda Bi'u na da karin bayani.

Rahoton harin Maiduguri da Potiskum
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:12 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG