Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ranar Laraba Firayinministan Burtaniya David Cameron Zai Yi Murabus


Firaministan Burtaniya David Cameron ya ce gobe Labara ne zai yi murabus a hukumance, wanda zai sa Ministar Cikin Gida Theresa May ta zama shugabar kasar ta gaba.

"Ta na da karfin gwiwa, ta kware, tana da duk wani abin da kasarmu za ta bukata na shugabanci a shekarun dake tafe, kuma zan goyi bayanta," a cewar Cameron a wata maganar da yayi da manema labarai jiya Litini.

Cameron ya ce gobe Labara zai halarci zaman Majalisar Dokoki na yin tambayoyi ga Firaminista.

"Bayan nan zai tafi Fadar Sarauniya in mika takardar aje aiki, saboda mu samu sabuwar Firaminista a wannan ginin da ke baya na da yammacin gobe Laraba," a cewarsa.

Da ana kyautata zaton da May da Ministar Makamashi Andrea Leadsom, su ne za su yi takarar a jami'iyarsu ta 'yan rikau ta 'Conservative,' wajen maye gurbin Cameron, wanda ya bayyana shirinsa na yin murabus, bayan ya kasa shawo kan 'yan Burtaniya su zabi zama cikin kungiyar Tarayyar Turai a zaben raba gardamar da aka yi a watan jiya.

XS
SM
MD
LG