Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shahararriyar Ma’aikaciyar Gidan Talabijin Na NTA Aisha Bello Mustapha Ta Rasu


Hajia Aisha Bello Mustapha
Hajia Aisha Bello Mustapha

Kwararriyar 'yar jarida kuma tsohuwar ma’aikaciyar gidan talabijin na NTA, Aisha Bello ta rasu ranar Lahadi sai dai ba a bayyana sanadin mutuwar ta ba.

Marigayiya A’isha ta kware sosai a aikin jarida da shirye-shiryen talabijin.

Kafin rasuwarta, Aisha ta rike mukamin babbar manaja a bangaren shirin Majalisa na gidan talabijin na NTA, bayan ta shafe shekaru 30 a matsayin mai gabatar da labarai.

Aisha ta fara aiki a NTA a matsayin mai daukowa da rubuta labarai, har ta kai matsayin mataimakiyar darakta a fannin labarai, sannan ta zama babbar manaja a fannin shirin 'yan majalisa na NTA. Aisha ta kasance daya daga cikin fitattun masu watsa shirye-shirye a NTA a daga shekarar aluf dari tara zuwa farkon shekara ta 2022 lokacin da ta yi ritaya.

Marigayiya Aisha Bello ta yi fice a matsayin matan arewacin Najeriya na farko da suka fara karanta labaran duniya da turanci a tashar talabijin ta kasa NTA, ta kuma zama abin koyi da alfahari ga matasan arewacin kasar da dama musamman 'yan jarida mata.

A wata sanarwa da ke dauke da sa hannun wani hadimin Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, Ajuri Ngelale, Shugaban kasar, ya bayyana Aisha a matsayin abin koyi da kuma alfahari ga mata. Shugaba Tinubu ya ce za a ci gaba da tunawa da yaba aikin da ta yi, yayinda ya kuma jajintawa 'ya'ya da iyalin da ta bari a baya.

Wakazalika ma'aikatar watsa labarai ta Najeriya ta wallafa sanarwar rasuwar tsohuwar 'yar jaridar da jajen shugaban kasa a shafinta na sada zumunta X.

Wadansu matasa sun bayyana jimamin rasuwar tsohuwar 'yar jarida a dandalin sada zumunta na X.

Marigayiya Aisha ta yi aiki na tsawon shekaru da dama da fitattaccen mai gabatar da labarai a tashar talabijin ta kasa NTA, Cyril Stober wanda ya yi ritaya a shekarar 2019.

Aisha ta sami horo a fannin aikin jarida a Jami'ar Ahmadu Bello ta Zari'a, inda ta sami digiri na farko a fannin harkokin sadarwa.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG