Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Faransa Ta Kai Hari Ta Sama Kan 'Yan Tawayen Mali


Kashmiri government employees demonstrate as riot police spray purple-dyed water during a protest march in Srinagar. Indian police detained dozens of government employees as they tried to stage a protest march demanding the regularisation of contractual jobs and an increase in salary.
Kashmiri government employees demonstrate as riot police spray purple-dyed water during a protest march in Srinagar. Indian police detained dozens of government employees as they tried to stage a protest march demanding the regularisation of contractual jobs and an increase in salary.

Sojojin Najeriya da na Senegal ma su na can kasar ta Mali domin dafawa sojojin gwamnati a kokarin murkushe 'yan kishin Islama da suka doshi kudu

Jiragen saman yaki na Faransa sun kai hare-hare a kasar Mali domin tallafawa sojojin gwamnati dake kokarin jan burki ma wasu mayaka ‘yan kishin Islama da suka doshi kudu.

Jiya jumma’a, ministan harkokin wajen Faransa, Laurent Fabius, ya tabbatar da kai hare-haren ta sama, amma ya ki bayarda karin haske game da wadannan matakan sojan.

Tun farko a jiya jumma’ar, Faransa ta ce ta aika da sojojinta zuwa Mali a bisa rokon gwamnatin kasar. Har ila yau, an tura sojoji daga Najeriya da Senegal zuwa Mali domin dafawa sojojin gwamnati.

Jami’an sojan Mali sun ce harin da aka kai ta saman ya ja burki ma ‘yan kishin Islamar. ‘Yan tawayen dake rike da dukkan arewacin Mali, sun kutsa kudu a wannan mako, suka kama garin Konna. Jami’an sojan Mali sun ce a yanzu dakarun gwamnati sun sake kwato garin.

Jiya jumma’a, shugaban rikon kwarya na Mali, Dioncounda Traore, ya ayyana dokar ta baci a kasar, ya kuma yi kira ga kowane dan kasar Mali da ya taimaka a wannan yaki.

Shugaba Francois Hollande na Faransa, yace sojojin Faransa su na taimakawa wajen yakar abinda ya kira gungun ‘yan ta’adda a kasar Mali.

Shugaban kasar Mali dai ya roki Faransa, wadda ta yi ma kasar mulkin mallaka, da ta kai musu daukin gaggawa don dakile farmakin ‘yan tawayen. Majiyoyin diflomasiyya sun ce Mr. Traore zai gana da shugaba Hollande a Paris ranar laraba mai zuwa.

Sakataren harkokin wajen Britaniya, William Hague, ya fada jiya jumma’a cewa Britaniya tana goyon bayan shawarar da Faransa ta dauka ta tsoma hannun sojojinta a rikicin Mali.
XS
SM
MD
LG