Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Tarayyar Afirka Ta Yi Maraba Da Dawowar Kasar Morocco


Tarayyar kasashen Afrika ta yi lale da dawowar kasar Morocco cikin kungiyar kasashen bayan fiye da shekaru 30 da kasar ta kwashe bata cikin tarayyar.

Duk da dai ba lallai bane dawowar kasar komai ya tafi daidai, shugabannin afirka sun ce hadin kan afrika ya fi muhimmanci a a wanna zamanin na canji da ake ciki a duniya.
A shekarar aluf dari tara da tamanin da 4 ne kasar morocco ta fita daga tarayyar saboda tarayyar Afrika ta yarda da samun ‘yancin yammacin yankin Sahara da aka yi ta takaddama akai.
Shugabannin Afrika sun ce a karshe, shawarar barin morocco ta dawo zabi ne na hadin kai da yarjejeniya.

XS
SM
MD
LG