VOA 60 Afirka - Junairu 08, 2013

Your browser doesn’t support HTML5

Yayin da ‘yan tawaye ke kara kusantar babban birnin Janhuriyar Afrika ta Tsakiya, shugaban kasar ya isa Brazzaville domin tattauna rigimar da shugaba Sassou-Nguesso.A kasar Cote ‘d Voire, shugaban asusun lamini na kasa da kasa Christine Lagarde yace rigima da makamai ne babban kalubalen cigaban Afrika a wani taro da ya hallarta a birnin Abidjan. Sabon shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama yayi Alkawarin hada kan kasa a bikin rantsar da shi. A Sudan kuwa, karo mai zaki na kara daraja a kasuwannin kasashen waje. A kayace mutan kasar Nijar suke, a fitowarsu ta biyu domin buga kofin kwallon kafa na nahiyar Africa da za’a fara a Afrika ta Kudu nan bada jimawa ba.