Iyalan Likitan Da Mayakan ISWAP Suka Yi Garkuwa Da Shi Sun Yi Kira Ga Gwamnati Ta Ceto Shi
Your browser doesn’t support HTML5
Iyalan likitan da mayakan ISWAP suka yi garkuwa da shi a Gubio a jihar Borno a watan Maris, sun yi kira ga gwamnati da ta yi duk mai yiwuwa don ganin an ceto shi. Matar likitan ta yi wannan kiran ne a wajen bikin ba da gidaje da kudi ga likitoci 81 a jihar da gwamnati ta yi.