Kasar Lao ta sami labarin farko na bullowar Cutar matsahashsararn Tsuntsaye

Mahukuntan kasar Lao sunce sun sami labarin bullar cutar mashassharan Tsuntsaye na farko cikin watanni 7 a kasar mai anu’in H5N1. Kakakin gwamnatin kasar Yong Chanthalangsy ya fada a a wannan makon cewa akallan tsuntsaye 17 ne suka mutu asakamakon kamuwa da kwayoyin cutar a kauyen Non Sawang dake wajen babban birnin kasar Vientiane. Yace akallan sun kashe maji da wasu tsuntsaye dubu daya, to amma a wasu lokutan cutar ta yadu zuwa ga dan Adam. Kamar yadda aka sani cutar dai ta kashe Mutane fiye da dari da sittin a duniya baki daya.