Ban Zabi Magaji Ba Sai Da Na Yi Istihara,Inji Gwamna Babangida

Gwamna Ma'azu Babangida Aliyu na jahar Naija

Gwamna Babangida Aliyu ya ce ta hanyar yin addu'a ya zabi Alhaji Umar Nasko

Gwamnan jahar Naija Ma'azu Babangida Aliyu na kan bakan shi na cewa lallai sai wanda ya zaba zai gaji kujerar gwamnan jahar duk kuwa da jayayyar da 'yan adawa ke ci gaba da yi da wannan mataki.

Gwamna Ma'azu Babangida Aliyu ya ce ba da ka fa ya ce sai Alhaji Umar Nasko ba, ya ce kafin ya furta sai da ya baiwa Allah zabi cikin mutane ishirin kamar yadda za ku ji a cikin rahoton da wakilin Sashen Hausa Mustapha Nasiru Batsari ya aiko daga Minna, jahar Naija:

Your browser doesn’t support HTML5

Gwamna Babangida ya ce Istikhara yayi kafin ya zabi magaji.-2':50"