Taron Kolin Amurka Da Afrika: Amurka Ta Ce Za Ta Sauya Yadda Take Hulda Da Afirka

Your browser doesn’t support HTML5

Bisa al’ada, kowace sabuwar gwamnati a Amurka ta na bullo da manufofi a game da yadda huldarta da kasashen Afirka za ta kasance. Jami’an gwamnatin Joe Biden sun kyankyasa cewa wannan taro, zai bude wani sabon babin kawance tsakanin Amurkar da nahiyar.