Tsamin Dangantaka Tsakanin Ghana Da Burkino Faso Ya Shafi 'Yan Kasuwar Ghana Masu Ratsa Burkino Faso

Your browser doesn’t support HTML5

Dangantaka tsakanin Ghana da Furkino Faso ta yi tsami biyo bayan kalaman shugaba Akufo-Addo a Amurka a bara cewa Burkina Faso ta dauko sojojin haya daga Rasha. Tun bayan nan 'yan kasuwar Ghana da ke dauko albasa daga Nijar sun yi ta fuskantar karuwar hare-hare akan hanyarsu a Burkina Faso.