Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

🔴 Kai Tsaye

Zaben 2023 a Najeriya

Dan takarar jam’iyar APC, Bola Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa bayan ya sami kashi 36% na kuri’un da aka kada a zaben shugaban kasa da aka gudanar ranar asabar, yayinda dan takarar jam’iyar PDP Atiku Abubakar ya zo na biyu da kashi 30% dan takarar Jam'iyar Labour Peter Obi kuma ya zo na uku da kashi.26%.

Tinubu ya doke sauran ‘yan takara goma sha takwas da kuri’u APC-8,794,726, yayinda dan takarar jam’iyar PDP Atiku Abubakar ya sami kuri’u 6,984,520, Peter Obi na jam’iyar Labour ya sami kuri’u 6,101,533, yayinda dan takarar jam’iyar NNPP-Rabi’u Musa Kwankwaso 1,496,687.

04:37 Maris 01, 2023

APC-8,794,726

PDP-6,984,520

LP-6,101,533

NNPP-1,496,687

04:33 Maris 01, 2023

Shugabanni a yankin yammacin Afirka sun bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC da ta bi tanade-tanaden dokar zabe ta 2022 dangane da tattara sakamakon zaben shugaban kasa da na 'yan Majalisar dokokin kasar da aka gudanar a ranar Asabar.

Wakilan kungiyar dattawan Afrika ta Yamma (WAEF) ne suka yi wannan kiran a Najeriya, ciki har da tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan da tsohon shugaban Ghana John Mahama, a wata sanarwa da suka fitar jiya Talata a Abuja.

Shugabannin sun kuma yi kira da a kwantar da hankula a kasar, tare da yin kira ga INEC da ta magance matsalolin da masu ruwa da tsaki daban-daban suka gabatar dangane da harkokin zabe.

02:37 Maris 01, 2023

APC-12

PDP-12

LP-12

NNPP-1

01:38 Maris 01, 2023

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kammala sanar da sakamakon zaben Shugaban kasa da turawan zabe suka tattaro daga jihohi.

Da yake sanar da kammala sanar da sakamakon zaben a daidai karfe daya da minti goma sha tara na dare, Shugaban Hukumar Zabe Farfesa Mahmood Yakubu ya nuna takardun da zasu cika da ya kunshi tattara adadin sakamakon zaben da aka kawo daga jihohi kafin sanar da jam'iyar da ta lashe zabe, da za a yi dukan a daren yau.

01:22 Maris 01, 2023

APC-66,406

PDP-30,234

LP-360,495

NNPP-1,552

01:08 Maris 01, 2023
An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Yadda A Amurka Ake Amfani Da Jirage Marasa Matuki A Hidimar Yau Da Kullum
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:31 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
An Kaddamar Da Wani Shiri Na Afuwa Ga Makiyaya A Kenya Da Suka Dawn Da Makamai
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:06 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Muhimmancin Samun Auduga Mai Inganci Ga Yara Mata A Lokacin Da Suke Al'ada
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:02 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Lafiyarmu
XS
SM
MD
LG