Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wakilan Yankin Niger Delta Sun Kauracewa Taron Sake Fasalin Siyasar Nijeriya


Wakilai daga yankin kudancin Nijeriya mai arzikin man fetur sun kauracewa zama na karshe na babban taron sake fasalin siyasar kasar da aka yi wata guda ana gudanarwa, a saboda rashin jituwa kan yadda za a raba dukiyar mai a kasar.

Wakilan da suka fito daga yankin Niger Delta sun fice daga zauren taron a yau litinin a bayan da aka ki biya musu bukatar da suka nema ta a ba su akalla kashi 25 daga cikin 100 na dukkan kudin da za a samu daga man fetur a kasar.

Wakilai daga sauran sassan kasar sun yarda ne kan cewa za a bai wa jihohin wannan yanki kashi 17 na dukkan kudin mai, watau karin kashi 4 daga cikin 100 daga kashi 13 da ake ba su a yanzu.

Ana fama da rashin kwanciyar hankalin a yankin na kudancin Nijeriya, har ma kungiyoyin sojojin sa kai a yankin sun yi barazanar yin tawaye idan har ba a kara yawan arzikin man da ake ba su ba.

Wannan taro na sake fasalin siyasar Nijeriya ya kunshi 'yan siyasa, da 'yan rajin kare muradu dabam-dabam da kuma shugabannin addini daga fadin kasar, kuma an shirya shi ne da nufin kawo shawarwari a kan yin gyara ga tsarin mulki.

XS
SM
MD
LG