Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Sanda A London Sun Nemi Gafarar Iyalan Wani Dan Kasar Brazil Da Suka Bindige Har Lahira


Babban baturen ’yan sanda na birnin London ya nemi gafarar iyalan wani mutumi dan kasar Brazil wanda ’yan sanda suka kashe a lokacin da suka ce sun zaci dan harin kunar-bakin-wake ne, amma kuma iyalan mutumin sun ce tuba kawai ba ta biya ba.

Babban jami’in rundunar ’yan sandan London, Ian Blair, ya bayyana takaicinsa ga iyalan mutumin a wata hirar da aka watsa yau lahadi, amma kuma ya ce za a ci gaba da yin aiki da umurnin da aka bai wa ’yan sanda na harbewa tare da niyyar kashewa, a bayan hare-haren kunar-bakin-wake na ’yan kwanakin nan.

An kashe Jean Charles de Menezes dan kasar Brazil mai shekaru 27 da haihuwa ranar Jumma'a a lokacin da aka ce ya gudu wa ’yan sanda masu fararen kaya a wata tashar karkashin kasa. Wani dan’uwansa yayi watsi da furucin babban jami’in ’yan sandan yana mai bayyana kisan a zaman rashin iya aiki na ’yan sanda.

Gwamnatin Brazil ta nemi cikakken bayani, kuma ministan harkokin wajenta yana ganawa da jami’an Britaniya a London kan wannan harbi.

A halin da ake ciki, ’yan sanda sun tayar da nakiyar da suka dasa jikin wata jakar da ba su yarda da ita ba a wata unguwar dake arewa maso yammacin London. Jami’ai suka ce watakila wannan jaka tana da alaka da hare-haren bam na kwanakin nan.

XS
SM
MD
LG