Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Robert Mugabe Yayi Barazanar Kawo Karshen Tattaunawa Da 'Yan Hamayya


Shugaba Robert Mugabe na Zimbabwe yayi barazanar tsinke tattaunawar raba iko idan har shugaban 'yan hamayya Morgan Tsvangirai ya ki yarda da mukaman da za a ba bangarensa a ganawar da za a yi litinin din nan.

Kafofin labarai na gwamnatin Zimbabwe sun ambaci Mr. Mugabe yana fada lahadi cewa, "ko dai su amince da abinda za a ba su, ko kuma iyakar lanmarin ke nan." An shirya mutanen biyu zasu gana litinin.

Morgan Tsvangirai, shugaban jam'iyyar hamayya ta MDC, ya sanya hannu a kan yarjejeniyar raba iko da Mr. Mugabe a watan Satumba. Amma an kasa aiwatar da yarjejeniyar a saboda sabanin ra'ayi a kan yadda za a raba muhimman ma'aikatu a tsakaninsu.

Mr. Tsvangirai ya doke Mr. Mugabe a zaben shugaban kasa da aka yi a watan Maris. Amma gwamnatin Mr. Mugabe ta ce bai samu fiye da rabin dukkan kuri'un da aka jefa ba, saboda haka ta ce a sake gudanar da zaben fitar da gwani a watan Yuni. Tsvangirai ya janye daga zaben na fitar da gwani, yana mai fadin cewa ana kashe magoya bayansa da yawa.

XS
SM
MD
LG