Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wata Kungiyar Sojojin Sa Kai Ta Kafa Sabuwar Gwamnati A Kudu Maso Yammacin Somaliya - 2002-04-02


Wata kungiyar sojojin sa kai ta kafa gwamnati ta 'yan tawaye a kudu maso yammacin Somaliya, yanki na uku da ya bijirewa gwamnatin rikon kwaryar da aka kafa a birnin Mogadishu.

'Ya'yan wannan kungiya mai suna "Rahanwein Resistance Army" sun sanyawa yankin nasu da sunan kasa mai zaman cin gashin kai na Kudu Maso Yammacin Somaliya. A jiya litinin kuma, suka nada shugaban soji, Kanar Hassan Mohammed Nur Shatigudud, a zaman shugabansu.

Somaliya ta kasa samun gwamnatin tarayya mai dorewa tun bayan faduwar gwamnatin marigayi Mohammad Siad Barre a shekarar 1991. An shirya gudanar da babban taron sasantawa na al'ummar Somaliya nan gaba cikin wannan wata a kasar Kenya.

Sauran yankuna masu cin agshin kansu da suka ayyana ballewa daga Somaliya sune Somaliland a arewa amso yammacin kasar, da kuma Puntland a arewa maso gabas.

XS
SM
MD
LG