Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wa'adin Da Yugoslaviya Ta Bai Wa Wadanda Ake Tuhuma Da Aikata Laifuffukan Yaki Ya Kusan Cika - 2002-04-19


Wa'adin da hukumomin Yugoslaviya suka bai wa mutane 23 da ake tuhuma da aikata laifuffukan yaki yana karatowa cikin sauri. A ranar laraba ne hukumomins uka bai wa wadannan mutane wa'adin kwanaki uku na su mika kansu ko kuma a kamo su karfi da yaji.

Biyu daga cikin mutanen da aka fi nema ruwa a jallo, watau tsohon madugun Sabiyawan Bosniya, Radovan Karadzic, da babban kwamandan sojojinsa, Janar Ratko Mladic, suna cikin jerin sunayen, tare da shugaban jamhuriyar Serbia na yanzu, Milan Milutinovic.

A jiya alhamis, babbar lauyar gabatar da kararraki a gaban kotun Shari'ar Laifuffukan Yaki ta MDD, Carla del Ponte, ta tattauna da jami'an Yugoslaviya a birnin Belgrade, domin matsa lambar da a mika mutanen dake tsare ko aka kama zuwa birnin Hague.

Hukumomin tarayyar Yugoslaviya sun buga jerin sunayen mutanen mako guda a bayan da majalisar dokoki ta zartas da dokar da ta bai wa gwamnati ikon mika mutanen da ake tuhuma zuwa kotun ta MDD.

XS
SM
MD
LG