Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu Musulmi Sun Kona Ofishin Jaridar 'This Day' A Kaduna... - 2002-11-20


Musulmi masu zanga-zanga sun kona ofishin wata jarida, a bayan da suka fusata da wani rahoton da jaridar ta buga cewar Annabi Muhammad (saw) yana iya auren daya daga cikin masu takara a gasar sarauniyar kyau ta duniya ta zamo matarsa.

Gungun Musulmi sun yi caa a kan ofishin jaridar "This Day" a garin kaduna yau laraba suna rera wakokin Musulunci yayin da suka kona ginin.

Babu wanda ya ji rauni a wannan lamarin.

Nijeriya tana daukar bakuncin gasar zaben sarauniyar kyau ta duniya ta bana wadda za a yi cikin watan Disamba a Abuja. Wata kungiyar Musulmi mai suna Kungiyar Ulama ta roki shugaba Olusegun Obasanjo da ya hana gudanar da wannan gasa.

A ranar asabar jaridar ta buga labarin cewa Musulmi suna dauka cewar abu ne maras kyau a gayyato mata 92 zuwa Nijeriya domin tallata tsiraiinsu, ta kuma ce ai da wannan zamanin Annabi Muhammad (saw) ne, ta yaya za a dauki wannan batu. Jaridar ta ci gaba da cewa watakila da auren daya daga cikin masu gasar zai yi.

Tuni dai jaridar ta nemi gafarar buga wannan labari.

XS
SM
MD
LG