Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shirin Tsagaita Wuta Na Fuskantar Tangarda Yayin Da Isra'ila Ta Kashe Falasdinawa Hudu - 2003-06-25


Kungiyoyin kishin Falasdinu sun lashi takobin daukar fansar hare-haren da suka kashe Falasdinawa hudu a yau laraba, abinda ya kawo tababar yiwuwar kulla shirin tsagaita wuta da Isra'ila.

Bangaren soja na kungiyar Hamas ya ce zai dauki fansa kan Isra'ila a saboda hare-haren da suka kashe membobinta biyu yau laraba a yankin Beit Hanoun na zirin Gaza.

haka kuma a yau laraba manyan shugabannin kungiyoyin kishin Falasdinu suka musanta rahotannin cewa sun yarda da tsagaita wuta na wucin gadi, suna masu fadin cewa har yanzu ana ci gaba da tattaunawa.

A wani gefen kuwa, Isra'ila ta kai hare-hare ta sama a zirin Gaza ta kashe wasu Falasdinawan biyu ta raunata 14. Isra'ila ta ce ta kai harin ne kan 'yan Hamas wadanda, a cewarta, suna shirin kai farmaki kan wata unguwar share ka zauna ta yahudawa a zirin Gaza.

XS
SM
MD
LG