Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Nada Sabon Sarkin Musulmi a Najeriya


A yau Alhamis, hukumomi a Najeriya suka baiyana Kanar Muhammadu Sada Abubakar na uku, a matsayin sabon Sarkin Musulmi, bayan rasuwar yayansa, marigayi Ibrahim Muhammadu Maccido, a hatsarin jirgin saman Lahadin da ta gabata.

Shekarun Sarki Muhammadu Sada Abubakar kimanin hamsin da haihuwa, kuma yana rike da mukamin Jami'in Huldar Tsaro na Najeriya a kasar Pakistan, lokacin da wannan sarauta ta fado masa.

A cikin aikace-aikacen da yayi na soja, har da aiki tabbatar da zaman lafiya a kasar Saliyo.

Kamar Sauran iyaye da kakanninsa, Sarki Muhammadu Sada Abubakar, jikan Shehu Usman Dan Fodiyo ne, mutumin da ya kada daular Musulunci ta Usmaniyya a shekarar 1804. (kimanin shekaru dari biyu da biyu kenan da suka wuce).

Sarki Muhammadu Sada shine Sarkin Musulmi na ashirin, tun daga kan kakansa Shehu Usman Dan Fodio.

XS
SM
MD
LG