Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar Kiyaye Hakkin Bi'adama Ta Majalisar Dinkin Duniya Tana Kira Ga Isra'ila Ta Janye Kawanya Datakeyiwa Zirin Gaza


Shugabar Hukumar Kula da hakkin Bil'adama ta Majalisar Dinkin Duniya tace kawanya da Israila take yiwa Zirin Gaza tana hana mazauna yankin hakkin da ya wajaba a baiwa ko wani bil'adama.

Kwamishina Mai kula da hakkin Bil'adama ta MDD,Navi Pillay, yau Talata tayi kira cikin gaggawa ga Isra'ila da ta janye killace yankin da tayi.Bayan haka sai a fara aikin jinkai mai karfin gaske domin saukaka abinda ta kira mummunar matsin rayuwa da mazauna Gaza suke fama dashi.

Pillay tace mutane miliyan daya da rabi dake zaune a Gaza an hanasu hakkinsu wadda kai tsaye ya saba dokokin kasa da kasa na 'yancin bil'adama.

XS
SM
MD
LG