Jam'iyyar
adawa ta Zimbabwe tace uwargidan Firayim Minista Morgan Tsvangirai ta rasa ranta,
shi kuma Prime Ministan ya sami raunuka a wani hatsarin mota da ya rutsa da su.
Kakakin
Jam'iyyar MDC yace motar da Morgan Tsvangirai tare da uwargidansa, Susan da mai
kare lafiyarsu da direba suke ciki, tayi taho mu gama da wata babbar mota a yau
Juma'a, a kan wani titi, dake kilomita hamsin, daga babban birnin kasar Harare.
Ita dai matar a nan take ta mutu.
A
wata hira da yayi da manema labarai, kakakin MDC Nelson Chamisa bai tabbatar da
mutuwar Susan kai tsaye ba, amma dai yace hadarin yayi muni kwarai, ya kuma ce
Mr. Tsvangirai ya sami raunuka.
Babu
bayanin halin da sauran mutanen dake tare da shi a cikin motar suke ciki.
Dukkansu dai an garzaya da su zuwa wani asibiti a birnin Harare.
Kafofin
MDC sunce Mr. Tsvangirai yana kan hanyarsa ne ta zuwa wajen wani taron gangami
da aka shiorya yi a gobe Asabar, a lokacin da suka gamu da hadarin.
A
halin da ake ciki kuma, 'yan sanda sun kame alkalin da a shekaran jiya ya bayar
da belin babban jami'in jam'iyyar hamayya, kuma wanda Prime Minista Tsvangirai
ya so ya nada Minista.
Hukumomi
sunce ana zargin Majistare Livingstone Chipadze da laifin wuce gona da iri,
saboda ya kyale lauyan Roy Bennet ya shigar da takardar neman beli a ranar
Laraba.
Ba
a dai saki Bennet ba, kuma Kotun kolin Zimbabwe ta yi watsi da belin na Majistaren
ya bayar, sannan tace a ci gaba da rike Bennet gidan wakafi har sai an sa
ranarb tuhumar cin amanar kasa da ake masa.