A Karon Farko, Tun Lokacin da aka Tsige Shi, Tsohon Gwamnan Jihar Adamawa yayi Magana

Murtala Nyako, gwamnan Jihar Adamawa

Tun lokacinda Majalisar wakilan jihar Adamawa ta tsige shi, tsohon gwamnan jihar Adamawa Murtala Nyako ya zanta da 'yan jarida

A karon farko tun lokacinda wakilan Majalisar wakilan jihar Adamawa suka tsige shi, kuma ya arce zuwa wata kasar waje, jim kadan bayan an tsige shi, tsohon gwamnan jihar Adamawa Murtala Nyako ya zanta da wasu kafofin yada Labaru

A zantawar da yayi da wakilin sashen Hausa, Ibrahim Abdulaziz, tsohon gwamnan ya yabawa zaben Janaral Mohammadu Buhari a zaman dan takara shugaban kasar na jam'iyar APC.

Gwamnan ya kuma tabo batun kalubalan matakan tsaro a Nigeria.

Ya kuma yiwa, wanda ya gaje shi shagube, inda yace dashi bai samu, an tsayar dashi dan takarar gwamna ba, bale na neman mukamin wakilin Majalisar dattijai.

Your browser doesn’t support HTML5

TOHON GWAMNAN JIHAR ADAMAWA MURTALA NYAKO