Hadakar kungiyoyi a jihar Taraba ta koka da tura karin sojoji a jihar, saboda fargabar da mutane suka shiga a shirye shiryen zaben da za a yi gobe.
A cigaba da daukar matakan tsaro da rundunar 'yansandan Najeriya ke yi, Sfeto-Janar din 'yansandan Najeriya Mohammed Adamu ya shawarci duk wani mai bindiga ya mika ta ga hukumar kafin ta je karbowa da kanta.
A yayinda ya rage kasa da sao'i 48 a gudanar da zaben shugaban kasa a Najeriya, shugabannin al’umma a yankin kudancin Najeriya na ci gaba da kira ga 'yan kasa musanmman matasa dasu fito domin kada kuri’unsu domin samun nasarar zaben.
Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya ta INEC tace jami’iyyun siyasa zasu ci gaba da yakin neman zabe kamar yanda doka ta tanadar. Hukumar zaben ta bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ta shirya a birnin tarayyar Najeriya Abuja.
Rundunar 'yan sandan jihar Ebonyi ta ce an maido da zaman lafiya a garin Izzi, bayan barkewar wani rikici tsakanin magoya bayan jam'iyyun APC da PDP a farkon wannan makon, wanda ya yi sanadiyar kone wasu gidaje, da asarar dukiyoyi.
Masu fashin baki da masana a fannin tsaro a Najeriya sun yi nazarin kalaman Shugaba Muhammadu Buhari, inda ya ce duk wanda aka kama ya sace akwatin zabe ya yi a bakin ransa, kalam sun kuma ja hankalin wasu da ke ganin ba daidai ba ne shugaban ya yi wannan huruci.
Yayin da Najeriya ke fuskantar zabe a ranar Asabar mai zuwa, rundunar soji ta shida da ke Fatakol a jihar Rivers, sun gano ana shirin yin amfani da wasu bata gari domin ta da hankalin masu jefa kuri'a ranar zabe.
Tshohon mataimakin shugaban kasar Najeriya kuma dan takarar shugaban kasa karkashin jam'iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana kwarin gwiwar cewa shi zai lashe zaben shugaban kasa da za'a yi ranar Asabar mai zuwa.
A yau Talata ne shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar plato, ya tabbatar da cewa za'a gudunar da zaben 2019 a garin Quanpa, bayan offishin hukumar ya kama da wuta ya yin da wasu katunan mutane da kayan aiki suka kone.
Tuni dai jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta ce za ta ci gaba da kamfen biyo bayan dage zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin tarayya zuwa ranar asabar 23 ga watan nan.
Domin Kari