Afghanistan: Taliban Na Fatan Kammala Tattaunawa Da Amurka

Zaman tattaunawa tsakanin Amurka da Taliban a Qatar

Tawagar Amurka ta samu jagorancin jami’in diplomasiyya Zalmay Khalilzad, wanda ba’amurke ne dan asalin kasar ta Afghanistan

Kungiyar Taliban ta ce tana fatan a yau Lahadi za a kammala tattaunawar da take yi da Amurka, wacce za ta ba da damar a cimma matsaya kan yadda za a kawo karshen yakin Afghanistan da aka kwashe shekaru 18 ana yi.

Zaman tattaunawan tsakanin bangarorin biyu da ke takaddama, wanda ake yin shi a karo na tara, ya gudana ne a inda aka saba yin taron, wato kasar Qatar da ke yankin tekun Fasha.

Tawagar Amurka ta samu jagorancin jami’in diplomasiyya Zalmay Khalilzad, wanda ba’amurke ne dan asalin kasar ta Afghanistan.

A jiya Asabar, kakakin Taliban Zabihulla Mujahid, ya fadawa Muryar Amurka cewa, bangarorin biyu suna kokarin shata yadda dakarun da Amurka ke jagoranta za su janye daga kasar ta Afghanistan.