Sakataren harakokin wajen Amurka Antony Blinken da ke ziyarar wuni biyu a jamhuriyar Nijar ya sanar da karin kudaden tallafi ga kasashen yammaci da tsakiyar Afrika wadanda za'a yi amfani da su don inganta rayuwar al’umomin wadannan kasashe.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya isa Jamhuriyar Nijar a yau Alhamis 16 ga watan Maris inda zai tattauna da takwaransa Hassoumi Massaoudou ( Hasumi Masa’udu) kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu masu dadaddiyar huldar diflomasiya.
Takwas ga watan Maris din kowace shekara, rana ce da ake bikin mata ta duniya inda taken bana ya mai da hankali kan bukatar samar da daidaito a tsakanin jinsi.
Jami'ar gwamnatin Biden da ke da alhakin kula da sojojin Amurka ta bayyana dabarun dakile duk wata barazanar yaki, tare da yin nasara daga kasar China, idan bukatar hakan ta zo.
Kwanaki biyu gabannin babban zabe a Najeriya, Sashen Hausa na Muryar Amurka ya gudunar ta taron mata zalla don wayar da kansu da kuma ilimantar dasu game da zaben, ganin cewa mata sune suka fi yawa wajen kada kuri’a a lokacin zabe bisa la’akari da zabukan baya.
Hukumar kula da kafafen labarai na ketare ta Amurka wato USAGM, ta hori wakilan kafafen labaru na Najeriya kan yadda za su tsare dokokin aikin jarida idan sun tashi ba da labarai kan yadda za a gudanar da babban zabe har zuwa bayan sanar da sakamako.
A shekarar 2000 aka kebe ranar 21 ga Fabrairu, a matsayin ranar bukin harshen uwa ta duniya (IMLD).
A ciki da wajen birnin New Orleans na jihar Louisiana da ke Amurka, ranar Talata ne za a gudanar da babban bikin Mardi Gras, lokacin bukukuwa na tsawon makonni da aka saba yi a al’adance.
“Amurka ta ce ba ta goyon bayan kowane ‘dan takara a zaben Najeriya. Ta ce ita dai babban muradinta shi ne ta ga an gudanar da ingantaccen zabe, na gaskiya mai cike da adalci, wanda kowa da kowa zai na'am da shi”
Shugaban Amurka Joe Biden ya fada a jiya Talata cewa, labarin Amurka labari ne na ci gaba da jajircewa, yayin da yake jawabi a kan halin da kasa ke ciki da ya maida hankali a kan manufofin tattalin arzikin na cikin gida, inda ya kara da kira ga ‘yan adawa na Republican da su hadu su yi aiki tare.
Sojojin Amurka sun ce sun kakkabo wannan baban bala-balan din kasar China na leken asiri a yankin gabar tekun Carolina.
A wani mataki na nuna goyon baya ga tsarin dimokaradiyya a Naijerya, Amurka ta sanya takunkumin bulaguro ga mutanen da ke da hannu wajen yin zagon kasa ga dimokradiyya a Najeriya
Domin Kari
No media source currently available
Dr. Sa'adou Habou, likitan kwakwalwar a sashen dake kula da masu tabin hankali a babban asibitin Maradi, ya yi mana karin bayani a game da lalurar ta’ammali da miyagun kwayoyi.
An bullo da wata sabuwar fasahar aikin likita inda ake amfani da na’urar VR wajen taimakawa marasa lafiya samun saukin radadi mai zafi sosai da kawar da damuwa, da ma taimakawa wajen haihuwa.
A cewar wani sabon binciken da aka buga a mujallar Lancet, tsakanin kaso 38-50 cikin 100 na marasa lafiya dake fama da cutar kyandar biri wato mpox na duniya suma suna fama da cuta mai karya garkuwar jiki.
Wata cibiyar kula da wadanda suka yi fama da tu’amalli da miyagun kwayoyi a birnin Maputo tana taimaka wa wadanda suka daina shaye-shaye su ɗauki matakan farko na murmurewa daga matsalar.
Wata malamar makaranta a Kumasi, Ghana ta na taimakawa wajen magance matsalar rashin zuwa ‘ya’ya mata makaranta, ta hanyar samar mu su da audugar mata da za ta taimaka mu su yayin da suke al’ada.
Domin ganin kasar ta iya show kan kalubalen shirya bikin baje kolin fina-finai na FESPACO karo na 28 da yanayin tabarbarewar tsaro ya yi mummunan tasiri akai, gwamnati Burkina Faso ta sa hannu sosai a cikin wasu fina-finai da ake yi a kasar.