An Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Karo Na Biyar A Jihar Naija

Wani wanda cutar shan inna ta gurguntar yana jawabi wajen wani taro

An kaddamar da Rigakafin yaki da ciwon shan inna karo na biyar a jihar Minna, Najeriya.

A cikin jawabinsa wajen kaddamar da rigakafin da aka gudanar a garin Tagina dake yankin masarautar Kagara, wakilin Hukumar Lafiya ta duniya, Mr. Bolaji Buhari ya bayyana cewa, kananan yara ishirin da biyar ne suke dauke da cutar a Najeriya a halin yanzu.

Wakilinmu Mustapha Nasiru Batsari da ya halarci bukin, ya ruwaito cewa, yau Jumma’a ne za a ci gaba da aikin rigakafin, har ya zuwa talata sha takwas ga wannan wata.

Your browser doesn’t support HTML5

Rahoton Rigakafin Shan Inna A Jihar Naija:1:40