An Kafa Wata Rundunar Tsaro Ta Musamman a Jihar Nasarawa

Masarautar Doma da ke jihar Nasarawa ta bukaci al’umma ta taimaka wajen bai wa dakarun Najeriya bayanai da zasu kai ga kakkabe bata gari da samar da zaman lafiya a Najeriya.

A ranar Litinin ne Shelkwatar dakarun Najeriya ta kaddamar da tubalin gina wata shelkwata ta musamman a karamar hukumar Doma, jihar Nasarawa, wadda za ta samar da tsaro, musamman a yankin Arewa ta tsakiyar Najeriya da ke fama da ayyukan bata gari.

Mai Martaba, Andoma na Doma a jihar, Alhaji Ahamadu Aliyu Kauga, ya bukaci jama’a su bai wa dakarun sahihan bayanai da za su taimaka a kokarin da ake na ganin an samar da dawamammen zaman lafiya.

Shugaban kungiyar matasan Fulani ta Miyetti Allah a Jihar Nasarawa, Alhaji Bello Dauga Inusa, ya ce kasancewar rundunar zai kawo karshen tashin hankalin da suke fuskanta.

Shugaban kungiyar matasan Tivi a Jihar Nasarawa, Peter Ahemba ya ce zasu ba dakarun goyon baya a wannan kokarin da ake yi na samar da zaman lafiya.

Saurari cikakken rahoton cikin sauti daga Zainab Babaji:

Your browser doesn’t support HTML5

An Kafa Wata Rundunar Tsaro Ta musamman a Jihar Nasarawa