An Kashe Mutane Uku a Yankin Bassa Na jihar Filato

  • Ladan Ayawa
An kashe wasu mutane uku a yankin Basa dake cikin jihar Filato amma sai dai ba a gane ko su wanene suka aikata wannan danyen aikin ba

An samu gawar wasu mutane uku a cikin karamar hukumar Basa dake cikin jihar Filato, wadanda ba a san wadanda suka kashe su ba.

Mataimakin shugaban kungiyar raya kabilar Iregwe, Aweze Doro yayi wa wakiliyar sashen Hausa Zainab Babaji bayanin yadda lamarin ya faru.

Yace yaran su dake aikin hakar kuza sun bar wurin aiki, suna hanyar dawowa gida sai wasu da ake zargin Fulani ne suka kawo musu hari akan hanya, inda suka kashe mutane uku take.

Doro yace ko a ranar littinin data gabata saida suka binne wani yaron su sakamakon irin wannan harin da Fulani suka kai musu.

Ga Zainab Babaji da karin bayani 3’03:

Your browser doesn’t support HTML5

An Kashe Mutane Uku a Yankin Basa na jihar Filato