An Rufe Kan Iyakokin Najeriya Da Kamaru

Sojojin Najeriya

An rufe kan iyakokin Najeriya da kamaru bisa yarjejeniya tsakanin kasashen da nufi kakkabe mayaka masu kaifin kishin Islama
Sojoji da suka karbi ragamar tsaron a jihohin Borno da Yobe da kuma Adamawa da aka ayyana dokar-ta-baci sun rufe kan iyakokin Najeriya da kasar Kamaru da nufin shawo kan mayakan da suka addabi jihohin bisa ga yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kasashen biyu.

Jami’an gwamnatin jihar Adamawa da suka hada da majalisar dokokin jihar sun yi kira ga al’umma su bada hadin kai su kuma kasance masu kiyaye doka da oda domin ganin an sami zaman lafiya cikin sauri abinda ake bukata kafin janye dokar ta bacin.

Your browser doesn’t support HTML5

An Rufe Iyakokin Najeriya Da Kamaru - 2:24