Ana Ci Gaba Da Samun Matsalar Man Fetur A Nigeria

  • Ladan Ayawa

Karancin man fetur a Najeriya, Mayu 26, 2015

Matsalar man fetur da akeci gaba da fuskanta a Najeriya ya haifar da cece kuce tsakanin kanfanin samar da man na (NNPC) da majilisar Dattijai.

Har yanzu ana ci gaba da samun matsalar man fetur a Najeriya.

Wannan yasa har aka shiga cece kuce tsakanin ‘yan majilisar Dattawa da kanfanin main a Najeriya wato (NNPC).

Kanfanin na NNPC tace shugaban kasa ya bada umurnin a rage farashin ga ‘yan kasa, sabanin yadda aka sawo shi.

Wannan batu ya harzuka ‘yan majilisar dattijai musammam masu kula da harkokin albarkatun mai na majilisar.

Ga Hassan Maina Kaina da Karin bayani

Your browser doesn’t support HTML5

Anaci Gaba Da Samun Matsalar Manfetur A Nigeria 2'23