Bamanga ya Dage Cewa ya na Nan Daram Kan Mukamin sa

Alhaji Bamanga Tukur, shugban jam'iyar PDP mai mulkin Najeriya

Baraka na kara fadada a jam'iyar PDP mai mulkin kasar Najeriya amma shugabannin ta na nuna cewa akasin hakan ke faruwa
Ko da yake alamu na dada nuna cewa kujerar shugabancin Alhaji Bamanga Tukur na ci gaba da tangal-tangal tare da kara fuskantar tarnaki da cin karo da matsalolin da watakila za su kai shi ga jefar da kwallon mangwaro ya huta da kuda, ko da yake har yanzu shi dai shugaban na jam'iyar PDP bai taba nuna cewa ya damu da wadannan matsaloli ba, kuma a duk lokacin da ya gana da 'yan jarida ya kan jadadda cewa ya na nan daran a kan mukamin shi.

Your browser doesn’t support HTML5

Bamanga ya ce ba inda zashi, ya na nan daram.-2':49"


Wakilin Sashen Hausa a Abuja Nsiru Adamu el-Hikaya ne ya aiko da rahoton.