Wadanda Suka Sace Damishi Sango Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 100

Mutanen da suka sace tsohon ministan wasanni na Najeriya, kuma shugaba mai ci na jam'iyyar PDP a Jihar Filato, Damishi Sango, sun bukaci da a biya su Naira miliyan dari kafin su sako shi tare da sauran mutane hudu da suka sace su jiya laraba da maraice.

Kakakin jam'iyyar PDP a Jihar Filato, Joseph Akansa, ya shaidawa wakiliyar VOA Hausa, Zainab Babaji, cewa barayin da suka sace tsohon ministan da wadanda suke tafiya tare, sun bar wata waya ta wani mukarrabinsa a cikin motar, wadda kuma ta wannan wayar suka sanar da jami'an tsaro irin bukatunsu.

An sace Damishi Sango tare da sauran mutanen a kusa da Jere a Jihar Kaduna, lokacin da suke kan hanyar zuwa Abuja daga Jos a bayan wani taron da suka yi game da babban taro na kasa na jam'iyyarsu da za a gudanar.

Ga cikakken bayanin sace mutanen da kuma irin matakan da suke dauka daga bakin kakakin jam'iyyar ta PDP a Jihar Filato, John Akans.

Your browser doesn’t support HTML5

An sace shuagban jam'iyyar PDP na jihar Filato - 1'57"