Baban hafsan hafsoshin sojojin Najeriya Janar Abayomi Olonisakin shi ya yiwa 'yan jarida bayanin sakamakon tattaunawarsu da shugaban kasa.
Yana mai cewa batun tsaro da duk abubuwan dake yiwa tsaro barazana an tattaunasu, kama daga satar mutane da rikicin manoma da makiyaya zuwa batun 'yan aware irin na Biafra duk sun tattauna, inji hafsan hafsoshin.
Shugaba Buhari ya basu umurni akan abubuwan da ya kamata su maida hankalinsu a kai sosai domin su samu nasarar aikace aikacensu a kasar.
Shugaban kasa yace kasancewar Najeriya kasa daya dunkulalla ba abun da za'a yi muhawara a kansa ba ne. Dole ne sojoji su yi aiki su tabbatar da kasar ta cigaba da zama kasa daya.
Alhaji Bello Arabi Sardaunan Damaturu daya daga cikin dattawan arewa maso gabashin Najeriya yana mai cewa ganawar da shugaban yayi gaskiya ce bisa ga yin la'akari da abubuwan dake faruwa a kasar. A yi maganin barazanar da 'yan Najeriya ke yiwa juna a samu a zauna lafiya.
Ga rahoton Hassan Maina Kaina da karin bayani.
Your browser doesn’t support HTML5