Shirin Da Dan Gari a wannan makon ya kai ziyara garin Yelwa mai nisan kilomita 7 zuwa 8 daga cikin birnin Jos babban birnin Jihar Filato.
WASHINGTON, D.C —
A wata hira da Suleiman Hassan na gidan rediyon Unity FM Jos, Sarkin Garin Yelwa na 4 Abdulhadi Umar, ya ce garin ya kai sama da shekara 300 da kafuwa kuma Hausawa ne suka kafa garin kafin zuwan turawa.