Da Dan Gari: Tarihin Zangon Atibobo, Ghana

Abdul'azeez Idi Kotoko na Alpha Rediyo Kumasi, ya yi hira da sarkin Zangon Atibobo mai Martaba Ufailu Dan Usman don jin dan takaitaccen tarihin Zangon.

Zangon Atibobo tsohon gari ne wanda ya shahara a matsayin Zango mafi girma a Ghana saboda a baya, wuri ne da ake cinikin bayi. Hausawa ne ke zama a garin, a cewar Ufailu.

Basaraken ya ce babban kalubalen da suke fuskanta shine yadda ake yi musu kallon baki, duk da cewa kakannin kakanninsu a Ghana aka haifesu, bayan haka suna fuskantar rashin ruwa.

Ga cikakken shirin cikin sauti.

Your browser doesn’t support HTML5

Da Dan Gari: Tarihin Zangon Atibobo, Ghana