Fulanin Kudancin Najeriya Sun Yi Taro a Ogun

Shanu

Fulani makiyaya na yankin kudancin Najeriya sun hadu sun tattauna a Ogun.

Fulani makiyaya dake jahohin kudancin Najeriya sun yi wani taro a jahar Ogun domin samar da zaman lafiya tsakanin su da manoma da kuma tsakanin su ya su Fulanin. Wakilin Sashen Hausa a shiyyar Ladan Ibrahim Ayawa ya hada rahoto akan taron na Fulani.

Your browser doesn’t support HTML5

Fulanin kudancin Najeriya sun yi taro. 2':27"

Ganin cewa da ma Fulani makiyaya na da kungiyar Miyetti Allah wadda ta yi fice a Najeriya, mahalarta taron na Ogun sun ce kungiyar su ta Jumnata Fulbe ba an kafa ta ba ne don ta maye gurbin Miyetti Allah ko ta yi ma ta shisshigi da katsalandan.

Suka ce aiki za su yi tare domin samar da zaman lafiya da fahimtar juna masu dorewa.