Gidajen Rediyon Kasashen Waje

Naurar rediyo

Matsalolin rashin kama tashoshin watsa labarai na kasashen waje
Matsalolin rashin kama tashoshin watsa labarai na kasashen waje, ya jawo kace na ce a Najeriya ganin irin yanda mutane ke ci gaba da nuna bacin rainsu game da diran mikiyar da sojoji cikin kwanakin nan ke yi akan wasu jaridun kasar.

Wasu ma’abota sauraren gidajen rediyon na cewa fiye da kwanaki hudu kennan basu samun kama gidajen rediyon kasashen waje ba batun da suke dangantawa da saka takunkumi ga ‘yan kasar.

Kungiyar wakilan kafofin yada labarai a kasar tayi tir da duk wani wunkuri na hana sauraren gidajen rediyon kasashen wajen.

Your browser doesn’t support HTML5

Gidajen Rediyo Kasahen Waje - 3'11"