Gwamna Kashim Shettima Ya Jinjinawa Matasan Civilian JTF

Gwamnan Jahar Borno, Kashim Shettima.

Har wa yau gwamnan na jahar Borno ya godewa matasan sannan yayi tir da halin wadanda ya kira "'yan siyasar Abuja".

Gwamnan jahar Borno Kashim Shettima ya ce gwamnatin sa a shirye ta ke ta ci gaba da tallafawa kungiyar matasan dake aikin tsaron sa kai da kuma aikin farauto 'yan Boko Haram da ake kira Civilian JTF.

Gwamnan na jahar Borno ya bayyana hakan ne lokacin da yake yin godiya ga matasan masu aikin tsaron sa kai saboda yadda suka sadaukar da rayukan su wajen ci gaba farauto 'yan Boko Haram.

Gwamnan ya ce da ba don kokarin wadannan matasa ba, da jahar Borno ba ta samu 'yar sa'idar da ta samu yanzu ba.

Ga rahoton da Haruna Dauda Biu ya aiko daga Maiduguri fadar gwamnatin jahar Borno:

Your browser doesn’t support HTML5

Gwamnan Jahar Borno ya Godewa Matasan Civilian JTF - 3'11"