Gwamnatin Kasar Nijer Na Neman Rage Farashin Kaya

wasu mata a kasuwa

Hukumomin kasar jamahuriyar Nijer sun gana da 'yan kasuwa a wani kokarin neman karya farashin kayan matsarufi albarkacin watan azumin Ramadan
Hukumomin kasar jamahuriyar Nijer na ci gaba da tattaunawa da masyu saye da sayarwa da nufin sawwaka farashin kayayyakin matsarufi a wannan watan na Ramadana. Ministan kasuwancin kasar malam Saleye Saidou ya gana da manyan 'yan kasuwa da kuma kungiyoyin fararen hula masu yaki da tsadar rayuwa a wani kokarin neman karya farashin kayayyaki ko talaka ya samu sa'ida. Wakilin sashen Hausa a birnin Niamey, Abdoulaye Mamane Amadou ya halarci taron, ga rahoton da ya aiko ma na:

Your browser doesn’t support HTML5

Gwamnatin Nijer na neman rage farashin kayan matsarufi albarkacin watan azumi - 2:08