An ci gaba da kokarin ceto mutane har ya zuwa yammacin jiya Talata a yankin Gofa, bayan zaftarewar kasa yayi sanadiyyar mutuwar akalla mutane 229 a kudancin kasar Habasha.
A yau talata hukumomin Habasha suka bayyana cewar, zaftarewa kasa a wasu yankunan kasar masu nisa sakamakon mamakon ruwan sama ta hallaka akalla mutane 157.
Masu fashin baki akan tafiyar siyasar duniya sun bi sahun sauran al'umma wajen bayyana matsayinsu dangane da matakin Shugaba Joe Biden na janye takararsa daga zaben Shugaban kasa na watan Nuwamban 2024.
Kungiyar likitoci ta kasa da kasa Medecins Sans Frontieres (Doctors Without Borders - MSF) ta ce fararen hula a Sudan suna fuskantar munanan tashe-tashen hankula a cikin sama da shekara guda da aka kwashe an gwabzawa tsakanin sojoji da dakarun sa-kai masu adawa da juna.
Shugaban kasar Sudan Abdel Fattah al-Burhan, ya karbi bakuncin jakadan Iran ranar Lahadi ya kuma tura nasa zuwa Tehran, a cewar gwamnatin kasar, don sake kulla dangantaka tsakanin kasashen shekaru takwas bayan tabarbarewarta.
‘Yan bindiga sun kai hari a kan iyakar Nijar da Najeriya, inda suka kashe mutane biyar tare da jikkata wani daya a garin Dambu da ke karamar hukumar Bazaga ta gundumar Birni N'Konni, sannan suka sace dabbobi da dama a garin.
Gwamnatin mulkin sojan Nijar ta bada sanarwar rage farashin man fetur da na diesel da nufin rage wa al’umma radadin tsadar rayuwa.
A wani samamen kasa da kasa da ya maida hankali akan kungiyoyin batagarin dake aikata laifuffuka a nahiyoyi 5 masu tushe a kasashen yammacin Afrika, ‘yan sanda sun kama mutane 300 sun kwace tsabar kudi dala miliyan 3 da toshe asusun banki 720, a cewar rundunar ‘yan sandan kasa da kasa ta Interpol.
Ruftawar wata haramtacciyar mahakar zinariya tare da birne mahakan da ransu ya hallaka akalla mutane 5 a arewacin kasar kenya, a cewar hukumomin yankin.
Yayinda al’ummar Musulmi a kasashe daban daban ke shagulgulan sallar Ashura a yau talata 10 ga watan Muharram, ‘yan shi’ah sun yi tattaki a birnin Yamai na jamhuriyar Nijar domin nuna juyayi akan kisan Imam Hussein, daya daga cikin jikokin annabi Muhammad S.A.W. da aka yi a Karbala dake kasar Iraqi.
Malawi ta sanar da cewa, ta kawo karshen barkewar cutar kwalara mafi muni a kasar, cutar da ta kashe kusan mutane 2,000 tun bayan bullar ta a watan Maris din shekarar 2022.
Domin Kari
No media source currently available