Gwamnatin Najeriya Ta Fitar Da Sharuda 6 Gabanin Bude Makarantu

Wasu dalibai a jihar Borno

Bayan da makarantu su ka shafe akalla watanni uku a garkame, gwamnatin Najeriya ta fitar da sharuda 6 yayin da ake nazarin bude su.

Karamin Ministan harkokin ilimi a kasar, Chukwuemeka Nwajiuba ne ya bayyana sharudan a birnin Abuja.

Sai dai ya jadadda cewa, ba sai makarantu sun jira izinin budewa ba kafin su fara shirye-shiryen bin wadannan sharudan.

A cikin wadannan sharudan guda shida, na farko akwai samar da wuraren wanke hannu a cikin kowacce makaranta.

Na biyu akwai samar da wuraren gwajin yanayin zafin jikin mutum a cikin makarantun.

Na uku akwai tabbatar da cewa akwai sinadaran kashe kwayoyin jikin dan adam a yawancın kofofi da kuma dakuna.

Haka kuma akwai mayar da hankali kan yanayin tsafta a cikin harabar makarantun, na karshe kuma ministan ya ce dole ne a bayar da tazara tsakanin mutane a cikin makarantun.

Ministan dai ya yi wa makarantu gargadi kan bude makarantu ba tare da izinin gwamnati ba.

A cikin makon da ya gabata ma an garkame wata makaranta a Kaduna bayan da ta bude ba tare da izinin gwamnati ba.

An dai rufe makarantun ne a duk fadin kasar bisa kokarin takaita yaduwar cutar Coronavirus wave ta addabi duniya gabadaya.

Ya zuwa yanzu dai wadanda suka kamu da cutar a Najeriyar ya kai 16,658.