Hukumomin Angola Na Zargin Dan Tsohon Shugaban Kasar Da Wawure $500m

José Eduardo dos Santos , tsohon shugaban kasa kuma mahaifin Filomeno dos Santos wanda aka zarga da wawure $500m daga babban bankin kasar

Mahukuntan kasar Angol sun hana dan tsohon shugaban kasar da gwamnan babban bankin kasar barin kasar

Hukumomin kasar Angola sun tuhumi Jose Filomeno dos Santos, dan tsohon shugaban kasar Edwardo de Santos, da aikata rashin gaskiya kan zargin tura dalar Amurka miliyan 500 daga babban bankin kasar zuwa Ingila.

Hukumomin kasar sun hana Jose barin kasar, haka nan tuhumar ta shafi tsohon gwamnan babban bankin kasar, shima an hana shi yin balaguro domin aiwatar da binciken kwakwaf akan lamarin.