Illar Bakon Dauro Ba Kuraje Bane

An kaddamar da aikin wayar da kan jama’a, game da allurar riga kafin cutar Bakon Dauro

An kaddamar da aikin wayar da kan jama’a, game da allurar riga kafin cutar Bakon Dauro, a jihar Neja.

Cutar Bakon Dauron dai na daya daga cikin cututtukan da hukumar lafiya ta duniya, ke fatan ganin an kawar da ita masamman a kasashe masu tasowa.

Dr. Fati Abdalla, darakta, a sashen riga kafin cututtuka na ma’aikatar lafiyar jihar Neja, ta ce illar Bakon Dauro, ga yaron da baida riga kafi ba wai kurajen dake fitowa a jiki bane, ya kansa yaro ya rasa muryarsa, ido ko ya samu tabuwar kwakwalwa ko kuma mutuwa.

A jihar Neja, dai akwai tarar Naira 50.000, ko daurin shekaru 5, ga duk wanda ya ki bari a yiwa yaronsa riga kafi. Za dai a fara yin wannan riga kafi ne a jihar Neja daga ranar 21 zuwa 25, ga wannan watan da muke ciki.