Kamfanin NNPC Zai Yi Wa Al'ummar Najeriya Aiki - Mele Kyari

Ginin NNPC a Abuja

Sabon shugaban kamfanin man fetur a Najeriya wato NNPC, Mallam Mele Kyari, ya sha alwashin bayar da himma wajen batun hako mai a arewacin Najeriya, baya ga wasu mashahuran sauye-sauye da ya ce zai aiwatar a tsawon wa’adinsa.

Mele Kyari ya kara da cewa za su tashi haikan wajen ganin cewa kamfanin NNPC ya yi wa al’ummar Najeriya muhimman ayyukan da su ka hada da samar da wutar lantarki da iskar gas, da inganta matatun mai domin samar da isasshen man fetur a fadin Najeriya baki daya.

Ya kuma yi alkawarin cewa nan ba da dadewa ba farashin man fetur zai sauka

Saurari cikkakiyar hirar cikin sauti.

Your browser doesn’t support HTML5

Mele Kyari: Zamu Tabbatar Da NNPC Tayiwa Al'ummar Najeriya Aiki