Karar Fashe-Fashe da Harbe-Harbe a Garin Bajoga

Jihar Gombe (File Photo).

Wani mazaunin garin Bajoga da ya tattauna da Sashen Hausa na Muryar Amurka cewa ana ci gaba da jin karar harbe-harbe da fashe-fashe a yankin arewacin garin.

Wani mazaunin garin Bajoga da ya tattauna da Sashen Hausa na Muryar Amurka cewa ana ci gaba da jin karar harbe-harbe da fashe-fashe a yankin arewacin garin, ta inda ofishin gunduma da kuma na yanki na rundunar 'yan sanda yake.

Malamin yace tun misalin karfe 7 na safiya 'yan bindigar suka shiga garin, a karo na biyu cikin 'yan watannin nan, amma babu bayani na takamammen inda suka kai ma hari.

Sai dai yace da ma an san cewa akwai sansanin 'yan Boko Haram a wasu 'yan kananan garuruwa da kauyuka da suke kusa da nan a tsallaken kogi, kuma har cikin garin su na shigowa sayen mai.

Ga bayanin tattaunawarsa da Sashen Hausa.

Your browser doesn’t support HTML5

Tattaunawar Sashen Hausa da Wani a Garin Bajoga Yanzun Nan - 4'32"