Kasim Moktar Ya Bayyana Dalilinsa Na Son Shugabancin Janhuriyar Nijar

  • Ibrahim Garba

Shugaban Janhuriyar Nijar

Da alamar dai siyasar Janhuriyar Nijar za ta kara armashi kwanan nan ganin Kassim Moktar ya bayyana aniyarsa ta shiga yakin neman zaben gadan-gadan

Shugaban jam’iyyar CPR Kasim Moktar ya bayyana dalilansa na neman zama shugaban Janhuriyar Nijar, wadanda su ka hada da abin da ya kira cigaba da gina alkibla da manufa da ka’idojin jam’iyyarsa, wadanda aka tsara su don bunkasa kasar.

Y ace da ikon Allah zai yi takarar Shugabancin kasar kuma ga dukkan alamu al’ummar Maradi da ma ta kasar baki daya za su goyi bayansa.

Alhaji Moktar y ace ko ya na da kwarin gwiwar cewa ba a Maradi ne kadai jam’iyyar da shi kansa ke da karbuwa ba, amma har ma a kasar baki daya. Y ace ko da ma kuri’u kadan su ka samu a Maradi, da yaddar Allah, babu abin da zai hana su yin takara.

Your browser doesn’t support HTML5

Kasim Moktar Ya Bayyana Dalilinsa Na Son Shugabancin Janhuriyar Nijar-2'26''