Kotun Kolin Najeriya Ta Saukar Da Sanatoci Biyu daga Nassarawa Da Anambra

Shugaba Goodluck Jonathan na Najeriya

Kotun kolin ta ce Solomon Ewuga shi ne sanatan halal na CPC daga Nassarawa ta Arewa ba Yusuf Musa Nagogo dake rike da kujerar ba

Kotun koli ta Najeriya ta kwace kujerar dan majalisar dattawa Yusuf Musa Nagogo dan jam’iyyar CPC mai wakiltar Nassarawa ta Arewa a Jihar Nassarawa, ta ba wani mai suna Solomon Ewuga, shi ma dan jam’iyyar ta CPC.

Haka kuma, kotun kolin ta tabbatarwa da uwargidar marigayi Chuba Okadigbo, tsohon shugaban majalisar dattawan Najeriya, Margarie Okadigbo, cewar ita ce ‘yar takarar halal ta jam’iyyar PDP daga mazabar Anambra ta Arewa, saboda haka, kujerar nata ne.

Nasiru Adamu El-Hikaya ya aiko mana da cikakken rahoto kan wannan daga Abuja...

Rahoton Nasiru:

Kotun Kolin Najeriya Ta Sauke Sanatoci Biyu