Kwamitin Bin Diddigi Yaje Chibok

Wasu iyayen daliban Chibok da aka sace.

Kwamitin bin diddigi akan daliban Chibok ya isa garin domin ganawa da iyayensu.
Kwanakin baya kwamitin yaje Maiduguri,da inyar zuwa chibok amma ya kasa zuwa saboda matakan tsaro.

Rade-radin da ake yi cewa an sako wasu ‘yan makarantar da ‘yan Boko Haram suke tsare dasu ba gaskiya ba.

Wakilin Muryar Amurka, Ibrahim Ahmed yace abunda ya faru shine lokacin da ake lissafin wadanda suka kubuto daga hannu yan bindiga akwai wasu dalibai guda hudu wadanda aka mata dasu.

Amma lokaci da kwamitin da shugaban kasa ya kafa domin bin diddigin abunda ra faru a chibok yazo Maiduguri, kwamishina ilimi na jihar Borno, Inuwa Lubo, ya gabatar da wadannan dalibai mata guda hudu a zamar cewa suna daga cikin wadanda suka samu suka kubuto daga hannun wadannan ‘yan bindiga.

Your browser doesn’t support HTML5

Kwamitin bin diddigi na garin chibok - 3'30"